Connect with us

News

Gwamna Kano Ya Umurci Kwamishinoni da Aka Canza Su Miƙa Dukkanin Takardun Da Suka Kamata Kafin Talata

Published

on

DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO 

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umurci dukkan kwamishinoni da aka sake musu wuraren aiki su tabbatar da gudanar da cikakken bayanai kafin ƙarshen ranar Talata, 17 ga Disamba, 2024.

Advertisement

Da yake magana ta bakin mai magana da yawunsa, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan ya bayyana cewa sauye-sauyen cikin majalisar zasu fara aiki ne gaba ɗaya a taron majalisa na gaba da za a yi ranar Laraba, 18 ga Disamba, 2024.

Gwamnan Kano Ya Umarci Kwamishinonin Da Aka Sake Musu Mukamai Da Su Tabbatar Sun Fara Aiki Kafin Ranar Talata

Ya jaddada muhimmancin kammala dukkan tsare-tsaren miƙa aiki kafin wannan lokaci.

Advertisement

 

“Dukkan kwamishinonin da sauyin ya shafa su miƙa wuya da sauya aiki tsakanin ranar Litinin, 16 da Talata, 17 ga Disamba, 2024,” in ji sanarwar.

Advertisement

Gwamnan ya ƙara jawo hankalin mambobin majalisar zartarwa ta jihar da su ƙara himma tare da rungumar ƙwazo, da jajircewa don ci gaba da tallafa wa gwamnatinsa wajen yi wa al’ummar Jihar Kano hidima.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending