News
An Bukaci Shugaban Tinubu Ya Fara Hukunta Ministocinsa Da Suke Kin Halartar Taruka – Majalissa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya bukaci Shugaban Kasa Bola Tinubu da ya gargadi Ministocinsa marasa rikon amana a cikin majalisarsa wadanda suka ki amsa gayyatar Majalisar Dokokin ba.
Akpabio ya ce irin wadannan ministocin da suka ki amsa gayyatar Majalissa basu dace da gurbin majalisar ministocin Tinubu ba domin girmama dimokradiyya.
Shugaban majalisar dattawan ya bayyana haka ne a ranar Larabar da ta gabata lokacin da shugaban kasar ya gabatar da kididdigar kasafin kudin shekarar 2025 na Naira Tiriliyan N47.9.gaban majalisar dokokin.
Wadanda suka yi watsi da gayyatar da Majalisar ta yi musu ba dimokuradiyya ba ne don haka ba su da gurbi a gwamnatin Shugaban Tinubu a cewar Akpabio a gaban ‘yan majalisar dattawa da na wakilai.
Ya kuma jadadda bukatar ministoci da Sanatoci su gaggauta amsa bukatun majalisar dokokin kasar domin bayar da bayanan da suka dace dangane da ayyukansu.
Shugaban majalisar dattawan ya ce ‘yan majalisar na da ikon da kundin tsarin mulki ya ba su na daukar mataki idan suka ki bayyana a gaban zauren majalisun biyu
Tinubu ya samu rakiyar Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), George Akume a wajen gabatar da kasafin kudin; da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila; da sauran manyan jami’an gwamnati.
Channel Tv
