News
Yan Sanda Sun Kama Matashi Da Laifin Garkuwa Da Ɗan Shekara 2 A Kano
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Rundunar ƴan sandan Kano ta ce ta kama wani ɗan shekara 25 mai suna Abubakar Musa bisa laifin garkuwa da wani ɗan shekara 2, Al’amin Ahmad Garba a jihar.
Matashin, wanda ɗan unguwar Rijiyar Lemo ne, ya nemi a biya shi Naira miliyan 50 a matsayin kuɗin fansa.
Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, acikin wata sanarwa da ya fitar ya ce a ranar 25 ga watan Disamba, 2024 ne aka kama wanda ake zargin bayan wani atisayen sirri da aka gudanar inda aka ceto yaron a yankin Unguwar Liman dake Ɗorayi bayan ɓoye shi na kwanaki uku da aka yi.
Daga nan ne aka garzaya da shi asibitin Murtala dake jihar don duba lafiyarsa wanda daga bisani aka damƙa shi ga ahalinsa.
Ya kuma ce an gurfanar da wanda ake tuhuma da laifin zuwa Kotun Shari’a dake Nomansland a ranar 3 ga watan Junairu wanda a halin yanzu aka tsare shi.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion7 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
