Connect with us

News

Rundunar ‘Yan Sandan Bauchi Ta Kama Wata Mata Bisa Zargin Kashe Kishiyarta

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wata mata mai suna Fatima Mohammed, mai shekaru 28, bisa zargin kashe kishiyarta Hajara Isa, mai shekaru 20, a unguwar Kofar Dumi da ke cikin birnin Bauchi.

Advertisement

Binciken farko ya nuna cewa wadda ake zargi ta shake Hajara har ta mutu, sannan ta yi kokarin boye laifinta ta hanyar zuba mata ruwan zafi da kona gawarta da buhun robobi.

Ma’aikatan KSIP Sun Koka Kan Rashin Biyan Su Mafi Karancin Albashi Na N71,000 A Kano

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa an fara gudanar da bincike na tsanaki domin tabbatar da an gurfanar da wadda ake zargi a gaban kotu.

Advertisement

Ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da baiwa hukuma hadin kai wajen bayar da sahihan bayanai domin tabbatar da zaman lafiya ajihar.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending