Connect with us

News

‎Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 40, Sun Kona Gidaje 383 A Filato ‎

Published

on

IMG 20250406 134913 scaled 1 750x430

‎A kalla mutane 40 ne suka rasa rayukansu, yayin da sama da mutane 1,000 suka rasa matsugunansu sakamakon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a makon jiya a kauyen Hurti da ke yankin Manguna a karamar hukumar Bokkos, jihar Filato.

‎Hakazalika, gidaje 383 ne aka kona kurmus, tare da lalata kayayyakin abinci da wasu kayayyakin amfanin yau da kullum.

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta buƙaci masu shirin zanga-zanga su sauya ranar yin gangamin

‎Hakkin wannan bayanin ya fito daga bakin Dagacin kauyen Hurti, Mista Maren Aradong, yayin da Sakataran Gwamnatin Jiha (SSG), Mista Samuel Jatau, ya jagoranci tawagar jami’an gwamnati domin duba barnar da aka yi.

Kamfanin Dallancin Labarai Kasa  (NAN) ya  tabbatar da cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki ne a ranar 2 ga Afrilu a kauyukan Hurti, Josho, Daffo da wasu kauyuka a yankin.

Advertisement

‎Gwamnan jihar, Kaleb Mutfwang, ya bayyana cewa hare-haren ba rikicin manoma da makiyaya ba ne,

‎Gwamnati ta tabbatar da kudirinta na kara tura jami’an tsaro a yankunan da lamarin ya shafa da kuma tallafawa wadanda suka rasa matsugunnai da ‘yan uwansu.

Advertisement

SOLACEBACE

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending