News
Kungiyoyi 87 Sun Mayar Da Martani Kan Zarge-Zargen Cin Hanci A Gwamnatin Kano
Kungiyoyin farar hula masu kishin Kano guda 87 sun yi watsi da wani jawabi da wata ƙungiya mai kiran kanta League of Civil Society Organisations ta fitar, wanda ta yi zargin cewa gwamnatin Kano ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf na tafiyar da mulki cikin cin hanci da rashawa a jihar.
A wata sanarwa da shugabannin ƙungiyoyin suka fitar a daren Litinin, mai ɗaukar nauyin haɗin gwiwar, Hassan Ibrahim Gama, da abokin aikinsa, Mustapha Muhammad Chiroma, sun bayyana wannan jawabi a matsayin wani yunƙuri na siyasa da farfaganda don bata sunan gwamnati.
Gidauniyar AMG Ta Fara Shirye-shiryen Samar Da Asusun Agajin Gaggawa A Kano
“Ya kamata CSOs, NGOs da CBOs a Kano su yi amfani da hanyoyin sa ido da ake da su a fannoni daban-daban kamar ilimi, lafiya, muhalli da kasafin kuɗi wajen tattaunawa da gwamnati ta hanyar gaskiya da hujja, maimakon dogaro da fafutukar siyasa,” in ji sanarwar.
Kungiyoyin sun ce, sun kula da jawabin League of CSOs na ranar 23 ga watan Agusta, 2025, wanda ya yi ƙoƙarin ɗora laifin cin hanci da rashin gaskiya kan gwamnatin jihar. Sun bayyana cewa kowanne ɗan ƙasa ko ƙungiya na da damar neman gaskiya, amma irin wannan jawabi, “ba wai kawai na wuri da ya gabata ba ne, har ma cike yake da siyasa, gangan-gangan, da kuma yunƙurin sauya wa jama’ar Kano tunani.”
Matsayar Kungiyoyin 87
1. Zargi Ba Hukunci Ba Ne: Sun ce dukkan shari’o’in da ake magana a kansu har yanzu na ƙarƙashin bincike ne a hannun EFCC da ICPC, kuma ba a iya yanke hukunci ta kafafen yaɗa labarai ko sanarwar manema labarai ba
2. Kano Na Samun Sauyi, Ba Lalacewa Ba: Sun ce gwamnatin Kano ta kaddamar da matakai na gaskiya, ciki har da cikakken bin ƙa’idojin bita da rahoton kuɗi, amfani da tsarin TSA, da kafa ofisoshin yaki da cin hanci a hukumomi.
3. Siyasantar da Kungiyoyin Farar Hula: Sun bayyana takaicinsu kan yadda League of CSOs ta bar kanta ga siyasa, suna mai cewa irin wannan yaɗa maganganu marasa tushe na iya hana masu saka jari shigowa Kano da kuma lalata kwarin gwiwar jama’a.
4. Hulɗar Gina Juna, Ba Fada Ba: Kungiyoyin sun ce gwamnati ta kasance a shirye don tattaunawa da masu kishin gaskiya, kuma sun bukaci sauran ƙungiyoyin su nemi bayanai a hanya mai gaskiya.
Kungiyoyin sun ce zarge-zargen da ake yi ba su wakilci gaba ɗaya gwamnatin Kano ba, kuma “ayyukan wasu ’yan tsiraru da ake bincike ba za su lalata tsarin gwamnati ba.”
Sun kuma bayyana cewa jihar Kano ba ta cikin “rudani” kamar yadda wasu ke yaɗawa, illa ma tana kan hanyar gyare-gyare, ci gaban zamani da shigar da al’umma cikin mulki.
Kungiyoyin sun bukaci al’ummar Kano su yi taka-tsantsan, su guji yada jita-jita, tare da goyon bayan gyare-gyaren gwamnati.
Sun kuma shawarci hukumomin yaki da cin hanci su ci gaba da aikinsu “ba tare da tsoro ko son rai ba, amma ba tare da barin farfaganda ta shafi aikinsu ba.”
Kungiyoyin 87 ɗin sun bayyana cewa sun ɗauki wannan matsayi ne don kare gaskiya, adalci da muradun jama’ar Kano.
1
Farouk Umar
Citizens for Development and Education (CDE)
2
Peter Hassan Tijani
Network for Empowerment and Development Initiative (NEDIN)
3
Yahaya A. Yahaya
National association of persons with physical disabilities Kano Chapter (NAPWPD)
4
Hassan Ibrahim Gama.
Masses First International Organization -MFI
5
Wali Ado Rano
Voice of the Hopeful Enlightenment and Development Initiative (VOHEDI)
6
Nworisa Michael
Stand For Peace Initiative
7
Dr. Kabir Hamisu Kura.
Community Development Initiative
8
Rakiya Abba Tahula
Interfaith Peace Foundation
9
Dr. Ramatu Garba
Support for Women and Teenage Children (SWATCH)
10
Maimuna Umar Sheriff
Centre for Gender Base Violence Advocacy
11
Ahmad Tijjani
Alkali Ahmad Center For Development
12
Ibrahim Muhammed
Rural – Urban Slums Development Initiative (RUSDI)
13
Abubakar Shariff Jaddah
Society for Women and Child Health Initiative (SWACHI)
14
Saratu I. Maigida
Lifeline Initiative For Widows Empowerment and Economic Development (LIWEED)
15
Ali Suleiman
Friends of the Community Organization (FOCO)
16
Halima Titi Bello
Women Gender Developers (WOGEND)
17
Dr. Yahaya Danjuma
International Peace and Secure Society (IPSS)
18
Safayanu Bichi
Kano Budget Working Group
19
Mustapha Muhammed Chiroma
Community Rights Initiative of Nigeria (CORIN)
20
Abdulrahman Uba Daushe
Spinal Cord Injuries Association of Nigeria (SCIAN)
21
Rakiya Ladi Musa
Ansar Women Development
22
Sabo Bello Madaki
Kiru Community Development Association
23
Sunusi Hashimu
Society for Child Support and Economic Empowerment (SOCSEE)
24
Samaila Namadi Ahmad
Yadfulde kiru local government Association and development
25
Asaju KolawoleKola
Kola and Funke Care Foundation
26
Ruth Stephen
Touch and Care Foundation (TOCAF)
27
Bashir A Bashir
Diamond Youth For Community Development
28
Salisu Gambo Ditol
Youth mobilization by media
29
Dr. Auwalu Halilu
Non-formal Development for Education and Health Initiatives ( NDEHI)
30
Dr. Tanimu Adam Ibrahim
Gwarzo Initiative Forum
31
Ola Taiwo
Mari-Care Foundation for Widows, Single Parents, Orphans and Vulnerable Children Nigeria. (MARI-CARE)
32
Suleiman Idris
Northern Youth Assembly
33
Mohammed Hussaini
Nigerian Democracy Working Group
34
Haj. Aisha Ahmed Abdulkadir (Dangi)
Sustainable Diana mic and Human Development Initiative
35
Gharzali Ibrahim Ungogo
Ummatee Centre for the Promotion of Public Education, Accountability and Social Safety (Ummatee-C4PASS) –
36
Rabi Yusuf Gezawa MON
Center For Empowerment Of Older Persons And The Vulnerable (CEOPAV)- Formally know as GADIAC
37
Mustapha Muhammed
Social Awareness and Community Development Initiative (SACDI Nigeria)
38
Prof Muhammad Bello Shitu
Inclusive Community Education and Development Association ( ICEADA)
39
Ismail Kanye
KABO Local Government Development Forum
40
Bello Karaye
Karaye Initiative Forum
41
Sani Bello Madaki
Kiru Community Development Association
42
Hassan Musa Yaro
Cardinal and Development Support Initiative
43
Maimuna Shu’aibu
Muna Helping Hand Foundation
44
Aisha Halliru
Halliru Memorial Youth Development and Empowerment initiative (AYDI)
45
Yusuf Muhammad Anas
Dawaki Youth Network for Better Tomorrow Initiatives
46
Abdurrashid Salisu Baba
Tsakuwa Mu Farka Development Association
47
Umaima Muhammad.
Aminci Multipurpose Development Association.
48
Hassan Jibril
Gano Development Association
49
Nusaibatu Muhammad
Iyayen Giji Development Association.
50
Adamu Balarabe Sarbi
Sarbi Development Association
51
Abdurrazak Ayuba usaini
Minjbir East Community Development Association(Mecda)
52
Zubairu Bala
Kwarkiya Youth Mobilization Forum
53
Ismaila Abdullahi
Gidan Kankara City Community
54
Audu Saidu
Mu Tallafi Juna Kadawa (B) Gwale Local Government
55
Umar Iliyasu Madobi
Madobi Youth Development Forum
56
Nura Lambu
Tofa Youth Development Forum
57
Shehu Isah
Gajida Youth Development Associations
58
Abdulaziz Habibu Bello
Yanoko Youth Development Association
59
Suleiman Lawan
Gulu Community Development Association
60
Ubale Yusuf
Kofar Gabas Development Association
61
Dalhatu Jibrin Dalhatu
Karaye Initiative Forum
62
Abubakar Auwal Ahmad
Diso Self Help Group ( DISHEG) Gwale Local Government
63
Murtala Muhd Rabiu
Hannu Dayawa Youth development Association Bachirawa – Ungogo Local Govt
64
Habibu Barau Ruwantsa
Ruwantsa Youth Development Association, Dambatta
65
Sulaiman Yusuf Maitama
Dambatta Reporters
66
Kabiru Balarabe Dambatta
Dambatta Academic Forum
67
Auwal Idris Dorayi
Center for Peace and Environmental Justice CEPEJ
68
Garba Lawan
Rano Development Association
69
Adamu Umar
Rano Youth Enlightenment Forum
70
Auwal Ayuba
Toranke Educational care & support Association.
71
Aminu Sa’ad
Consolidated Ajingi Development Association.
72
Saminu Yusha’u Chula
Chula Area Development Association.
73
Abdullahi Madaki
Kunkurawa Youth Development
74
Sunusi Garba Shehu Gajale
Kafin maiyaki Community Development Association (KACODA), Kiru Local Government Area.
75
Ahmad Tahir
Doguwa Tailoring association.
76
Abdulrazaq Ado Zango
Kano Initiatives Of Persons With Special Needs (KIPSN)
77
Dr. Mustapha Mukhatar
Danbatta Development Forum (DDF)
78
Sani Shuaib Rogo
Rogo Concern Citizens
79
Amb. Abbas Abdullahi
Beyond Border Alliance (BBA)
80
Khadija Shehu Muhammed
Save the Future Initiative (SAFI)
81
Abubakar Abdulkadir
One Voice Development Initiative (OVID)
82
Lami Bako Yakasai
Enlightenment And Empowerment Of Northern Women Initiative
83
Solomon Samuel
Mercy Helpline Initiative
84
Barr. Mustapha Idris
Human Right and Community initiative. Contact person
85
Khadija A. Muhammad
Nana Aisha Development Initiative (NADI)
86
Isyaku Ahmad
Voice And Accountability Platform (VAP)
87
Bashir Adamu Jigirya
Participatory Learning and Action for Community Ownership (PLACO)_
