News
KATSINA:Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5
An samu sabon zaman tattaunawa tsakanin jami’an tsaro da tubabbun ƴan bindiga a fadin Jihar Katsina, inda aka samu tabbacin dakatar da hare-hare a ƙananan hukumomi guda biyar na jihar.
Tattaunawar zaman lafiyar, wadda ta gudana a ƙauyen Kakumi da ke ƙaramar hukumar Bakori, ta haɗa da: ƴan bindiga da wakilan ƙananan hukumomi guda biyar da abin ya shafa — Bakori, da Kankara, da Funtua, da Kafur, da Malumfashi.
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Dukkanin Jami’o’in Gwamnati Da Ke Najeriya.
Manufar tattaunawar ita ce ƙarfafa ƙoƙarin samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’ummomi da ƴan bindigar da suka amince su ajiye makamai. Rahotanni daga yankin sun nuna cewa shugabannin ƴan bindigar sun yi alkawarin dakatar da kai dukkan hare-hare a cikin waɗannan yankuna daga ranar Lahadi, 12 ga Oktoba.
Wannan mataki na zaman lafiya yana cikin shirin gwamnati na kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta daɗe tana hana noma, da kasuwanci, da zaman lafiya a yankin kudancin jihar. Manyan mutane, da sarakunan gargajiya, da jami’an tsaro sun halarci taron, inda suka roƙi kowa da kowa da ya tsaya kan yarjejeniyar domin amfanin kowa.
Mazauna yankin sun nuna fatan cewa wannan sabuwar yarjejeniya za ta kawo dawwamammen zaman lafiya. “Muna roƙon Allah ya tabbatar mana da wannan zaman lafiya da tsaro,” in ji wani mazaunin yankin.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
