Connect with us

News

‎’Yan Bindiga Sun Yi Ajalin Jami’an Sa Kai 16 Tare Da Yin Garkuwa Da Mutane 42 A Neja ‎

Published

on

AFGHANISTAN UNREST TALIBAN

Akalla jami’an sa-kai 16 ne suka rasa rayukansu, yayin da ’yan bindiga suka yi garkuwa da mutum 42 a hare-haren da suka faru a ƙauyuka daban-daban na ƙaramar hukumar Mashegu dake jihar Neja tsakanin Lahadi 9 zuwa Alhamis 13 ga Nuwamba, 2025.

‎Mazauna yankin sun ce hare-haren sun haifar da tsananin fargaba, lamarin da ya sa dubban mazauna yin kaura daga gidajensu domin tsira da rayuka.

Advertisement

Ƙungiyar Ma’aikatan Lafiya Ta JOHESU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Najeriya

‎Wani mazaunin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce maharan sun fara kai hari ne a Dutsen Magaji a ranar Lahadi, inda suka sace mutum 22.

‎Ya ce, “Sa-kai sun bi su suka yi artabu da su. A wannan musayar wuta ne sa-kai uku suka mutu, mutane biyar kuma suna jinya.”

Advertisement

‎Sai dai, a cewar sa, ’yan bindigar sun dawo da sanyin safiya a ranar Alhamis, suka shiga ƙauyen Magama lokacin da jama’a ke cikin sallar asuba.

‎“Sun zagaye masallaci suka tafi da mutum fiye da 20. Wasu sa-kai sun bi sahunsu ba tare da sanin an yi musu kwanton bauna ba. ‘Yan bindigar suka bude wuta, inda sa-kai 13 suka rasa rayukansu,” in ji shi.

Advertisement

‎Mai magana da yawun shugaban ƙaramar hukumar Mashegu, Isah Ibrahim Bokuta, ya tabbatar da aukuwar lamarin. Ya ce jami’an sa-kai da suka mutu sun nuna jarumta wajen kare al’ummarsu, inda ƙaramar hukumar ta bayyana godiya kan jajircewarsu.

‎Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ce za su binciki rahoton kafin su fitar da cikakken bayani.

Advertisement

‎A yanzu haka, mazauna da dama daga ƙauyuka kamar Dutsen Magaji, Borin-Aiki, Gidan Ruwa da Magama sun bar gidajensu, inda ake ce musu suna neman mafaka a Mashegu, Kawo-Mashegu, Manigi da wasu yankuna.

‎A wani lamari daban, tsohon shugaban SUBEB na jihar Neja, Alhaji Alhassan Bawa Niworo, har yanzu yana hannun masu garkuwa, duk da labarin cewa iyalansa sun biya naira miliyan 70 a matsayin kudin fansa.

Advertisement

‎An sace Niworo tare da wasu jami’an gwamnati a ranar 29 ga Satumba, 2025, a kan hanyar Mokwa–New Bussa da ke ƙaramar hukumar Borgu.

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending