Connect with us

News

Gobara Ta Yi Ajalin Sama Da Mutum  80 Yayin Da Ke Ci Gaba Da Neman Mutane 250 Da Suka Bace

Published

on

74916700 803

Hukumomin Hong Kong sun ce mutanen da suka mutu a gobara mafi muni da ta auku a birnin sun kai akalla mutane 83 yayin da ma’ikatan kwana-kwana ke ci gaba da neman mutane 250 da suka bace.

Har yanzu hayaki na tashi a dogayen benaye takwas na rukunin gidajen da gobarar ta auku.

Advertisement

Prof. Gwarzo Donates 10 Million Naira, Two-Storey Building, Equips with Ultra-Modern Facilities for Alliance Française Kano

Hukumomin sun ce an kaddamar da bincike kan musabbabin aukuwar gobarar mafi muni da ba a taba ganin irinta ba cikin shekaru 80 a birnin kasuwancin inda suka ce suna binciken gyaran da ake yi a gidajen inda aka bar wasu abubuwa kamar ledoji da shingen roba a wurin wadanda ke iya kamawa da wuta.

Yan sanda sun ce sun kama mutane uku bisa zargin sakaci na barin abubuwan da ke iya kamawa da wuta a wurin da gobarar ta tashi

Advertisement

 

DW

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending