News
Yan Bindiga Sun Sake Yin Garkuwa Da Manoma 24 A Neja
Yan bindiga sun sake yin garkuwa da manoma 24, a gonar shinkafa da ke karamar hukumar Shiroro a Jihar Neja
Mazauna yankin sun ce maharan sun afka gonar ne da misalin ƙarfe 2:00 na rana, lokacin da manoman ke cikin aikin girbin amfanin gona na bana.
Duk da cewa ofishin soji na Erena na da nisan kusan kilomita biyar kacal daga yankin, ’yan bindigar sun tsere cikin sauƙi tare da mutanen da suka yi garkuwa da su, kafin jami’an tsaro su isa wurin.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda aka akayi garkuwa da su. A ranar da abin ya faru, wasu ’yan bindiga daban sun kutsa Kauyen Kakuru.
Advertisements
