Connect with us

News

Gwamnatin Jigawa Ta Tsige Alƙalin Kotun Musulunci Kan Rashawa

Published

on

Sharia law e1554378902662.jpg
Spread the love

Hukumar Shari’ah ta Jihar Jigawa (JSC) ta amince da tilasta wa alƙalin Kotun Shari’ar Musulunci da ke jihar yin ritaya.

Wannan na ƙunshe ne a wata takarda babban jami’in yaɗa labaran JSC, Abba Wangara ya fitar a yau Talata, a Dutse.

Muna Da Mamakai Masu Linzami Sama Da 250,000 Da Za Su Ishe Mu Yaki Har Na Tsawon Shekara Biyar —Inji Rundunar Sojan Iran

Advertisement

Haka kuma, hukumar ta amince da ƙarin matsayi ga wasu jami’anta guda 80 a muƙamai daban-daban.

Ya bayyana cewa, an ɗauki matakin ne yayin wani zama da hukuncin ta gudanar a Dutse.

A cewarsa, bayan bincike mai zurfi da samar da hujja mai ƙarfi akan ƙorafin da aka gabatar akan alƙalin, JSC ta yanke hukuncin tilasta wa Muhammad Haruna yin ritaya.

Advertisement

Ya ƙara da cewa, matakin ya biyo bayan miƙa ƙorafin ne da wani Abdullahi Hamza ya jagoranta, wanda ya yi sanadiyyar samun alƙalin da hannu a laifin rashawa da tsarewa ba bisa doka ba.

Wangara ya ce bincike ya nuna cewa alƙalin ya nemi wanda ya shigar da ƙorafin da biya wasu kuɗaɗe da ba sa bisa doka ba, don haka ya tilasta masa biyan wasu kuɗaɗe da tsare shi.

A watan Junairun 2025 ne JSC ta sallami jami’an shari’a bisa ayyukan saɓa wa dokokin aiki, shawartar wasu alƙalai uku da su yi murabus da kuma dakatar da wasu biyu daga aiki.

Advertisement

 

DAILY TRUST 

Advertisement
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *