Connect with us

News

Shari’o’in Zaɓe: Kotu Ta Kawo Sabon Tsari Don Kauce Wa Ƙarewar Wa’adi

Published

on

kotu 768x390 (1)

Babbar Kotun Tarayya ta Najeriya ta ba da umarnin fara karɓar ƙararrakin da suka shafi shari’o’in gabanin zaɓe a ranakun ƙarshen mako da kuma ranakun hutun musamman da gwamnati ke ayyanawa.

Wata sanarwa da Babban Magatakardan Kotun, Yahaya Shafa, ya sanya wa hannu ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin tabbatar da cewa masu ƙorafi da lauyoyinsu sun samu damar shigar da ƙararraki cikin wa’adin da doka ta tanada.

Advertisement

Sanarwar ta ce za a riƙa buɗe rajistar kotuna daga ƙarfe 10:00 na safe zuwa 2:00 na rana a ranakun Asabar da Lahadi, da kuma ranakun hutun da gwamnati ta ayyana.

Kotun ta ce manufar sabon tsarin ita ce kauce wa duk wani jinkiri da ka iya haifar da ƙarewar wa’adin shigar da ƙara, musamman a shari’o’in da suka shafi zaɓe, waɗanda doka ta ware musu takamaiman lokaci.

Advertisement

Matakin ya shafi shari’o’in da suka danganci zaɓukan fidda gwani na jam’iyyun siyasa, rikice-rikicen cikin gida na jam’iyyu da sauran batutuwan da suka shafi shirye-shiryen zaɓukan da ke tafe.

Masu sa ido kan harkokin shari’a na ganin cewa matakin zai taimaka wajen sauƙaƙa wa masu neman adalci da kuma tabbatar da cewa babu wanda zai rasa damar gurfanar da ƙorafinsa saboda ranakun hutu.

Advertisement

 

 

Advertisement

RFI

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending