News
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Mai Garkuwa Da Mutane Ne A Kano
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta sanar da cafke wani mutum mai suna Mohammed Isah Haruna, mai shekaru 28, bisa zargin hannu a ayyukan garkuwa da mutane da kuma kai wa ‘yan bindiga makamai da kayan sojoji.
Kakakin rundunar ya bayyana cewa an samu nasarar kama wanda ake zargin ne bayan wani ɗan ƙasa mai kishin al’umma ya kai sahihan bayanai ga jami’an tsaro cewa an ga wani mutum sanye da kayan sojoji cikin yanayi mai cike da shakku a ƙauyen Rimaye.
Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Cin Zarafin Ɗaliba A Gombe
Bayan samun rahoton, jami’an ‘yan sanda tare da haɗin gwiwar al’ummar Rimawa sun kai samame cikin gaggawa, inda suka cafke wanda ake zargin. A binciken da aka gudanar, an gano wata jaka a hannunsa da ke ɗauke da mujallar bindigar AK-47 guda ɗaya mai harsasai 30, ƙarin harsasai 79 na AK-47, kayan sojoji guda biyu, hulunan sojoji guda uku, katin shaidar soja na bogi, katunan shaida daban-daban, katunan ATM guda huɗu da kuma takalman sojoji na hamada.
Rundunar ta ce yayin gudanar da bincike, Mohammed Isah Haruna ya yi ikirarin cewa ya je yankin ne domin kai waɗannan kayayyaki ga wasu ‘yan bindiga da ke buya a cikin daji. Ta ce bincike ya ci gaba domin gano sauran waɗanda ake zargi da hannu a lamarin da kuma tabbatar da dukkan bayanan da aka samu.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa al’ummar Rimawa kan kishin ƙasa da haɗin kan da suka nuna wajen bai wa jami’an tsaro bayanan sirri. Ya jaddada cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ci gaba da yaƙi da masu aikata laifuka, tare da kira ga jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanan da za su taimaka wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
-
Opinion3 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News5 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
