News
Mutane 7 Sun Mutu A Mahakar Ma’adinai A Filato
Akalla mutane bakwai ne su ka mutu bayan ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a yankin Kassa da ke karamar hukumar Barkin Ladi a jihar Filato.
Shaidun gani da ido sun ce ma’aikatan hakar ma’adinai da dama sun kuma samu raunuka a ya yin faruwar lamarin.
Mutane 7 Sun Mutu A Mahakar Ma’adinai A Filato
Lamarin ya faru ne a yammacin ranar Laraba a ya yin da wadanda abin ya shafa ke gudanar da aikin hakar ma’adinai a wurin.
Wani mazaunin yankin, Albert Danlami, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:00 na dare.
Danlami ya bayyana cewa wadanda abin ya shafa sun makale a karkashin kasa biyo bayan ruftawar, lamarin da ya sa mazauna yankin da sauran ma’aikatan hakar ma’adanan su ka fara kokarin ceto mutanen.
Mai magana da yawun kungiyar matasan Berom Rwang Tengwong ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce ma’aikatan hakar ma’adanan bakwai ne su ka rasa rayukansu, inda ya ce an yi kokarin ceto ma’aikatan bayan faruwar lamarin, sai dai an dauko wasu ba tare da rai ba.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
