Connect with us

News

Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto

Published

on

IMG 20231117 WA0049 768x576 1

Ana fargabar mutuwar kusan mutane 40 bayan wani kwale-kwale da ke ɗauke da manoma da ma’aikatan aikin gona ya kife a garin Gorau, da ke ƙaramar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto.

Rahotanni sun ce kwale-kwalen na ɗauke da sama da mutane 70, ciki har da yara masu shekaru tsakanin 10 zuwa 15, lokacin da ya kife jim kaɗan bayan ya taso domin tsallaka wani rafi zuwa gonakin shinkafa.

Walƙiya Tayi Ajalin Mata Biyu, Ciki Har Da Mai Juna Biyu A Bauchi

An ce shugaban ƙauyen na cikin waɗanda suka shiga kwale-kwalen, amma daga baya aka samu nasarar ceto shi tare da wasu mutane.

Wani ɗan jarida da ya kasance a wurin, Sharhabilu Yahuza Kiliya, ya ce zuwa yanzu an gano gawarwakin kusan mutane 40, yayin da aka ceto mutum shida.

Ana ci gaba da aikin ceto da neman wadanda har yanzu ba a san inda suke ba, tare da kokarin gano sauran gawarwakin.

Advertisement

 

 

PLATINUM POST NEWS 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending