News
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
Ana fargabar mutuwar kusan mutane 40 bayan wani kwale-kwale da ke ɗauke da manoma da ma’aikatan aikin gona ya kife a garin Gorau, da ke ƙaramar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto.
Rahotanni sun ce kwale-kwalen na ɗauke da sama da mutane 70, ciki har da yara masu shekaru tsakanin 10 zuwa 15, lokacin da ya kife jim kaɗan bayan ya taso domin tsallaka wani rafi zuwa gonakin shinkafa.
Walƙiya Tayi Ajalin Mata Biyu, Ciki Har Da Mai Juna Biyu A Bauchi
An ce shugaban ƙauyen na cikin waɗanda suka shiga kwale-kwalen, amma daga baya aka samu nasarar ceto shi tare da wasu mutane.
Wani ɗan jarida da ya kasance a wurin, Sharhabilu Yahuza Kiliya, ya ce zuwa yanzu an gano gawarwakin kusan mutane 40, yayin da aka ceto mutum shida.
Ana ci gaba da aikin ceto da neman wadanda har yanzu ba a san inda suke ba, tare da kokarin gano sauran gawarwakin.
-
News5 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
News6 days ago
An Tura Kwamishinonin ’Yansanda 30 Da Jami’ai 15,000 Domin Sanya Ido A Zaɓen Osun
-
News4 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
