Connect with us

News

An sace jariri a wani asibiti a Bauchi

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hankula sun tashi a sashen masu haihuwa na Asibitin Koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi a arewa maso gabashin Najeriya, bayan da aka sace wani jariri.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa uban jaririn ya ce ƴan biyu matarsa ta haifa a ranar Laraba, sai wata mata ta yi shiga irin ta malaman asibiti ta ce wa matarsa ɗaya daga cikin jariran ba shi da lafiya za a duba shi a wani sashen na asibitin.

Advertisement

Ta Haifi Tagwaye Amma Kowa Mahaifinsa Daban

Daga nan ta ɗauki yaron ta tafi ba ta sake komawa ba.

Advertisement

Uban jaririn Ibrahim Dallami Khalid ya ce ya yi tsammanin matarsa ta san matar ne shi ya sa bai yi wata hoɓɓasa ba a lokacin da ya ganta.

“Daga baya bayan na bar asibitin sai matata ta cewa mahaifiyarta ta kawo mata ƙwai. Bayan ta tafi kawo ƙwan ne sai matar ta sake komawa ɗakin ta tambayi surukata ina za ta. Sai ta amsa mata ta wuce.

Advertisement

“Ita kuma matar sai ta yi amfani da damar ta zauna kusa da matata, ta ce mata ɗaya daga cikin jariran ba shi da lafiya za ta kai mata shi sashen da ake duba yara. Sai matata ta ƙyale ta ta ɗauke shi. Tun daga sannan ba a sake jin ɗuriyarta ba.”

Jaridar Daily Trust ta ce ta so jin ta bakin mai jegon amma ba ta cikin hayyacinta tun bayan faruwar lamarin.

Advertisement

Shugaban kwamitin ba da shawara na asibitin Dr. Haruna Liman ya bayyana lamarin a matsayin marar daɗi, kuma rundunar ƴan sandan jihar ta ce tuni ta ƙaddamar da bincike don kama wacce ake zargin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending