Connect with us

Sports

Neymar ya ce bai da hannu a badakalar komawarsa Barca daga Santos

Published

on

Neymar

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Dan wasan tawagar Brazil Neymar ya sanar da wata kotu a Sifaniya cewar bai da hannu wajen kulla yarjejeniyar komawarsa Barcelona daga Santos a 2013.

 

Advertisement

Dan kwallon da ke taka leda a Paris St Germain ya ce ya saka hannu kan kunshin kwantiragi kamar yadda mahaifinsa ya umarce shi.

FIFA 2022: Kizz Daniel zai cashe a ranar bude gasar cin kofin duniya na ƙwallon ƙafa

Advertisement

 

Ana tuhamar Neymar da wasu mutun takwas da aikata zamba da cin hanci – batun da suka musanta aikata ba daidai ba.

Advertisement

 

Wani kamfanin zuba jari DIS shi ne ya ke da mallakar kaso 40 cikin 100 na cinikin, amma sai ya tashi ba ko sisi, bayan makuden kudin cinikin kamar yadda aka sanar a duniya ya bambanta da wanda aka bayar.

Advertisement

 

Sauran da ake tuhuma sun hada da mahaifan Neymar da wakilan kungiyoyin biyu da tsoffin shugabannin Barcelona, Josep Maria Bartomeu da Sandro Rosell da tsohon shugaban Santos, Odilio Rodrigues.

Advertisement

 

DIS na son a daure Neymar shekara biyar, yayin da masu shigar da kara a Sifaniya ke fatan a garkame dan wasan Brazil shekara biyu da tarar yuro miliyan 10, suna kuma son a daure Rusell a kuma ci tarar Barcelona.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending