Connect with us

News

‘Sanin Darajar Auren Mata Masu Ilimi Ya Sa Zan Auri Gwarzuwar Musabakar Al-Qur’ani’

Published

on

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Fitaccen malamin addinin Islama, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana cewa sanin darajar ilimi ya sa zai auri wata Hafizar Al-Qur’ani a ranar Juma’a ta jibi.

 

Advertisement

Daurawa ya kuma ja kunnen wadanda suke yada hotunan kwalliyar matashiyar da zai aura da su daina wannan mummunar dabi’a.

Matashin Da Aka Sace Wa Babura Masu Kafa Uku Ya Kashe Kansa

Advertisement

 

Shehin Malamin ya bayyana cewa, hoton da ake yadawa na amaryar tasa a dakin babarta ana mata kwalliya wasu suka dauka ba a sani ba wanda hakan bai kamata.

Advertisement

 

A cikin wani katin gayyata da ke yawo a kafofin sada zumunta, ya nuna cewa Sheikh Daurawa zai angwance da gwarzuwar shekara a musabakar Al-Qur’ani ta kasa da aka gudanar tun a watan Maris na bana.

Advertisement

 

Gwarzuwar shekarar Haulatu Aminu Ishaq ta wakilci Jihar Zamfara a gasar Alkur’ani da aka yi ta kasa kamar yadda malamin ya bayyana a wata tattaunawarsa da Freedom Radio.

Advertisement

 

Malamin ya kuma kara da cewa, cin amana ne matuka yada hoton kwalliyar amaryar tasa, kuma ita kanta ba ta ji dadin hakan ba, wanda hakan ya sa ranta ya dugunzuma matuka, ta yi kukan bakin cikin yadda hoton kwalliyar  ya yi yawo a soshiyal midiya.

Advertisement

 

“Wannan duk ya san ya sa ya je ya goge domin kuwa sun aikata fasadi,” a cewar Daurawa.

Advertisement

 

Har wa yau, ya kara da cewa, sanin darajar auren mata masu ilimi ya sa zai auri wannan hazika a bangaren Kur’ani.

Advertisement

 

A karshe, Malamin ya kara da cewa da ma haka ya kamata attajirai da malamai su rika yi wajen aure ‘yan matan da suka nuna bajinta a bangaren addini ba a “shadaicin banza ba.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending