Connect with us

News

ICPC Ta Rufe Haramtattun Makarantu 62 Masu Bayar Da Shaidar Digiri

Published

on

Masu yi wa kasa hidima

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar Yaki da Rashawa da Sauran Laifuffuka (ICPC) ta ce ta rufe haramtattun manyan makarantu 62 a fadin Najeriya.

 

Advertisement

Kazalika, hukumar ta ce ta rufe wani sansanin masu yi wa kasa hidima (NYSC) na bogi da ta bankado.

An Dakatar Da Babban Sakatare Kan Satar Dizel A Ebonyi

Advertisement

Hukumar ta ce ta daukin matakin rufe wuraren ne a matsayin wani bangare na kokarin da take yi na yaki da rashawa a fannin ilimin kasar nan.

 

Advertisement

Shugaban ICPC, Farfesa Bolaji Owasanoye, shi ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi a wajen taron matasan da hukumar ta shirya a Abuja kan rashawa a manyan makarantu.

 

Advertisement

Da yake jawabi bisa wakilcin babbar jami’a a hukumar, Hannatu Mohammed, Owasanoye ya ce tuni an dauki matakin da ya dace a kan wadanda ke da hannu a wuraren da aka rufen.

 

Advertisement

Ya ce ICPC ta kafa kwamiti na musamman a makarantu domin yaki da rashawa, musamman a manyan makarantu.

 

Advertisement

Ya kara da cewa, kwamitin kan yi kokarin horar da mambobinsa kan nesanta kansu da rashawa da kuma cusa kyawawan dabi’u a zukatan takwarorinsu dalibai.

 

Advertisement

A nasa bangaren, babban mai jawabi a wajen taron, Farfesa Williams Barnabas, ya nuna bukatar bincikar dalibai masu son shiga manyan makarantu domin tabbatar da suna da cancantar da ake bukata.

 

Advertisement

 

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending