Connect with us

News

An Dakatar Da Babban Sakatare Kan Satar Dizel A Ebonyi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

 

 

 

Gwamnatin Jihar Ebonyi ta dakatar da Babban Sakataren Ma’aikatar Lantarki da Makamashi na Jihar, Mista Godwin Nwankwo, kan zargin satar man dizel da aka tanada don amfanin fitilun kan titi.

Advertisement

 

Kazalika, dakatawar ta shafi Hadimi na Musamman ga gwamnan jihar, Mista Emmanuel Nwangbo.

 

Likitoci dubu 24 ne suka rage a Najeriya – NMA

Kwamishinan Yada Labarai na jihar, Uchenna Orji ne ya shaida wa manema labarai haka jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwar jihar ranar Laraba.

 

Advertisement

Ya ce, “Majalisar ta amince da dakatar da jami’an biyu wadanda aikin kula da fitilun kan titi ke karkashin kulawarsa.”

 

Ya kara da cewa, Majalisar ta sami rahoton sace-sacen dizel da ake tafkawa karkashin masu kula da fitilun hanya.

 

Don haka ya ce, ta ta amince a gudanar da bincike kan badakalar ta hannun hukumar tsaro ta DSS domin gano wadanda ke da hannu a cikin sace-sacen.

 

Advertisement

 

 

 

 

 

AMINIYA

Advertisement

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending