Connect with us

News

Wasu yan bindiga sun Kone Wata Babbar Kotu A Ebonyi

Published

on

 

 

Advertisement

 

Wasu ’yan bindiga sun kone wata babbar kotu a yankin Owutu-Edda da ke Karamar Hukumar Afikpo ta Kudu a Jihar Ebonyi.

Advertisement

 

An ruwaito cewa ’yan bindigar sun mamaye kotun ne a ranar Talata, inda suka kone ta tare da lalata takardun cikinta.

Advertisement

Soja Ya Harbe Uwa Da Jaririnta A Kan Cin Hancin N200 A Neja

 

Rajistaran kotun, Oluchi Uduma, ta tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Owutu-Edda a ranar Laraba.

Advertisement

 

Ta ce ginin kotun da takardu da sauran kayayyaki masu amfani sun kone kurmus baki daya.

Advertisement

 

 

Advertisement

Shi ma Shugaban Karamar Hukumar ta Afikpo ta Kudu, Chima Nkama, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya kara da cewa an kai rahoton lamarin ga ’yan sanda.

 

Advertisement

Lamarin na Ebonyi ya kara haifar da kone-kone a yankin Kudu maso Gabas.

 

Advertisement

A watan Disamban 2022, wasu ’yan bindiga sun lalata wata kotun majistare da ke Owerri da kuma wata babbar kotu a Karamar Hukumar Orlu ta Jihar Imo.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending