Connect with us

News

Da Yawan Mukarraban Gwamnatin Buhari Kamata Yayi Ace Suna Kurkuku – SDP

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar SDP, Adewole Adebayo, ya ce idan har tsarin ‘yan sanda ya yi tasiri a Najeriya, rabin wadanda ke gwamnatin Buhari, za su kasance a gidan yari.

Advertisement

 

Ya bayyana haka ne a wani taro na biyu na yan takarar shugaban kasa da gidan talabijin na ARISE tare da hadin gwiwar Cibiyar Dimokaradiyya da Ci Gabanta (CDD) suka shirya.

Advertisement

 

NDLEA ta kama wani da take zargi babban dilan miyagun ƙwayoyi ne

Advertisement

Adebayo ya ce, “Kada mu gudu daga kafa gwamnati amatakin tarayya, akwai kundin tsarin mulki na taimakawa da zan rantsar da shi a ranar 29 ga Mayu.

 

Advertisement

A cikin kundin tsarin mulkin, yana da duk abin da ake bukata don kawar da laifuka.

 

Advertisement

“Kuma matakai biyu da za a bi don kawar da miyagun laifuka shi ne kawar da laifuka a cikin gwamnati, wannan shine abu mafi wahala a Najeriya.”

 

Advertisement

“Daya daga cikin dalilan da ya sa ba mu da ingantaccen tsarin ‘yan sanda shi ne, idan muna da ingantaccen tsarin ‘yan sanda, rabin wadanda ke gwamnati za su kasance a gidan yari.”

 

Advertisement

A karo na biyu na zauren taron akwai ‘yan takarar shugaban kasa hudu da suka halarta – Omoyele Sowore, na AAC. da Mallam Yabagi Sani, Farfesa Peter Umeadi, da Adebayo.

 

Advertisement

Taro na farko ya hada ‘yan takarar shugaban kasa guda hudu da aka zabo bisa la’akari da ayyukan jam’iyyunsu a wani bincike da CDD ta gudanar a yanar gizo.

 

Advertisement

Manyan jam’iyyun sun hada da Labour Party (LP), (APC), (PDP) (NNPP).

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending