Connect with us

News

Qatar 2022: Zakir Naik Na Halartar Gasar Kofin Duniya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Fitataccen mai wa’azin Musulunci dan kasar Indiya, Dokta Zakir Naik na halartar gasar kwallon kafar na Cin Kofin Duniya da za a soma a Qatar a ranar Lahadi.

 

Advertisement

Hakan ta bayyana ne bayan fitar hotunan Dokta Zakir Naik bayan saukarsa a filin jirgin sama na Doha, babban birnin kasar Qatar a ranar Asabar.

Yan sandan Kebbi sun ceto mutum bakwai da aka yi garkuwa da su

 

Advertisement

Zakir Naik ya lashe kyautar Sarki Faisal kan hidima ga Musulunci

Wasu bayanai sun nuna cewa mai Zakir Naik ya je Qatar ne a bisa gayyatar gwamanatin kasar na ya gabatar da wani majalisin wa’azi a yayin da ake gasar.

Advertisement

 

Qatar ta bijiro da wasu tsare-tsare na yada addinin Musulunci a yayin gasar Cin Kofin Duniya da ake sa ran mutum sama da mutane miliyan biyu da rabi za su halarta.

Advertisement

 

Wasu daga cikin tsare-tsaren sun hada da samar da wuraren Sallah da kuma wuraren alwala a filayayen wasa, abin da ba a taba yi ba a tarihin gasar a duniya.

Advertisement

 

Qatar ta kuma hana sayar da barasa a wuraren da za a buga wasannin.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending