News
Mahaifiya Ta Binne Jaririyar Da Ta Haifa Ranta A Cikin Masai
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
An kama wata mata mai kimanin shekara 30 da ke kauyen Tsurma a Karamar Hukumar Kiyawa ta jihar Jigawa bisa zargin binne jaririyar da ta haifa a cikin masai.
Da yake tabbatar da kamen, Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Lawan Shi’isu, ya ce tuni suka tono gawar jaririyar sannan suka cafke wacce ake zargin.
Arzikin Aliko Dangote ya ƙaru da dala biliyan 1.5 a watan Nuwamba
Ya kuma ce, “Bayan samun rahoton, mun aike da jami’anmu zuwa wajen, inda suka tono gawar daga cikin masan da ake zargin a ciki ta binne jaririyar.
“Yanzu haka mun cafke matar kuma tana hannunmu,” inji Lawan.
Kakakin ya kuma ce an garzaya da gawar Babban Asibitin Dutse, inda likita ya tabbatar da rasuwarta.
Ya kuma ce bincikensu na farko-farko ya kai su ga kama wani mai suna Amadu Sale da aka fi sani da Dan Kwairo mazaunin kauyen Akar a Karamar Hukumar ta Kiyawa, wanda shi ake zargi tun farko da yi mata cikin shege.
Ya ce bayan yi mata cikin, an zargi Dan Kwairo da hada baki da ita domin ta kashe yarinyar bayan ta haife ta.
Kakakin ya kuma ce tuni Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Emmanuel Ekot, ya ba da umarnin mayar da lamarin zuwa sashen binciken manyan laifuka na rundunar domin fadada bincike.
Ya ce da zarar an kammala binciken, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya domin su girbi abin da suka shuka
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
