Connect with us

News

2023: Amurka Za Ta Mara Wa Najeriya Baya A Harkar Zabe

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Gwamnatin Kasar Amurka ta ce za ta mara wa Najeriya baya dangane da zaben 2023 don tabbatar da masu kada kuri’a sun samu aminci a yayin zaben.

Advertisement

 

Amurka ta bayyana hakan ne ta bakin ofishin jakadancinta a Najeriya.

Advertisement

El-Rufai ya yi wa fursunoni 11 afuwa a Kaduna

 

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya rawaito Amurka za ta mara wa kasar baya ne karkashin shirin ‘Vote023’.

Advertisement

 

Vote023 shiri ne na musamman don wayar da kan jama’a kan harkokin zabe musamman ganin yadda zaben 2023 ya karato.

Advertisement

 

Daya daga cikin jagororin shirin ‘Vote023’, Misis Angela Ochu-Baiye ce ta bayyana haka ranar Asabar a Legas.

Advertisement

 

Ochu-Baiye ta ce abin a yaba ne ganin Ofishin Jakadancin Amurka ya amice su yi aiki tare don wayar da kan ’yan kasa kan zaben 2023.

Advertisement

 

(NAN)

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending