Connect with us

Sports

Kungiyoyi Da Dama Sun So Dauka Ta Amma Na Yi Wa Al-Nassr Alkawari —Ronaldo

Published

on

DAGA HASSAN KHALID HAMZA

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Cristiano Ronaldo ya ce kungiyoyin kwallon kafa da dama a sassan duniya sun nuna sha’awar daukar sa amma ya yanke shawarar sanya wa Al-Nassr hannu.

 

Advertisement

A lokacin da Al-Nassr ta gabatar da shi a matsayin dan wasanta a gaban dubban magoya bayan kungiyar a ranar Talata, Ronaldo ya bayyana cewa kungiyoyi a nahiyar Turai da Brazil Amurka da Australia da Portugal sun nemi su dauke shi amma ya zabi zuwa Saudiyya.

Binciken SIYASA: Baizama lalle Tunubu yaci Kano ba

 

Advertisement

“Kamar yadda na fada a baya wannan dama ce a gare ni ba wai a harkar kwallon kafa ba, dama ce da zan sauya tunanin matasa masu tasowa.

 

Advertisement

“Kungiyoyi da dama daga Nahiyar Turai da Brazil da Amurka da Australia da ma Portugal son so dauka ta amma na yi wannan kungiya alkawari.

 

Advertisement

 

“Na san abin da nake so da wanda ba na so, kuma wannan babban kalubale ne a gare ni na zuwa wannan kasa, ba don komai ba sai don na kara samun ilimi.

Advertisement

 

“Ina son sabon yanayi, kasa don cimma wani buri na daban tare sa Al-Nassr, wannan shi ne dalilin da ya sa na rungumi wannan dama,” in ji Ronaldo.

Advertisement

 

Ronaldo, dan shekara 37 a duniya, ya rattaba hannun zama a Al-Nassr na tsawon shekara biyu da rabi bayan raba gari da Manchester United a watan Nuwamban 2022.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending