Connect with us

News

Tankin ruwa na sama ya fado ya murkushe wani matashi

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

 

Advertisement

Tankin sama na ruwa da ake sanya wa a gidaje ya rikito kan wani matashi wanda sanadiyar haka ya rasa ransa.

Wannan lamari dai ya faru ne a unguwar Ikotun-Ekpe da ke birnin na Ikko.

Advertisement

Ƙalubale shida da ke gaban sabbin hafsoshin tsaron Najeriya

Gaskiya Ta Fi Kwabo ta ruwaito cew, Jamal Nureini mai shekaru 20 yana kwance ne a cikin daki a gidan su sai kawai tankin sama na ruwa na wani gida da ke makotaka da gidan su ya fado daga sama akan dakinsa da ya ke bacci, ya kuma bula kwanon dakin ya fado ya murkushe shi.

Kakar matashin Alhaja Yemisi Odejinmi wanda ta ke rayuwa da jikan nata a gidan, ta ce, wannan al’amari ya yi matukar sanya rayuwarta cikin garari.

Advertisement

“Ina kokarin idan Jamal ya tashi daga bacci za mu tafi fadar basaraken Legas don neman shaidar dan jiha saboda an bukaci Jamal da ya kawo a makaranta saboda ya samu gurbin karatu a jami’ar jihar Legas amma yanzu ga abin da ya faru” inji kakar marigayin

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending