News
Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Hukumar gudanarwar Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil (ADUSTECH) ta ce ba ta daukar ma’aikata, sabanin yadda kafafen sada zumunta ke yada cewa suna shirin daukar ma’aikata.
Malam Abdullahi Datti, mataimakin magatakardar yada labarai na ADUSTECH ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano ranar Litinin.
Ma’aikatan Hukumar NIPOST Sun Ki Yarda Da Shugaban Da Tinubu Ya Nada
“Mahukuntan jami’ar na sun bayyana a fili cewa labarin karya ne kuma ba shi da tushe, don haka ya kamata jama’a su yi watsi da shi,” in ji Datti.
Ya kuma yi kira ga jama’a da su daina yada irin wannan jita-jita da bata da tushe bare makama.
A Wani labarin kuma Ma’aikatan Hukumar NIPOST Sun Ki Yarda Da Shugaban Da Tinubu Ya Nada
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
