Connect with us

News

Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Hukumar gudanarwar Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil (ADUSTECH) ta ce ba ta daukar ma’aikata, sabanin yadda kafafen sada zumunta ke yada cewa suna shirin daukar ma’aikata.

Malam Abdullahi Datti, mataimakin magatakardar yada labarai na ADUSTECH ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano ranar Litinin.

Advertisement

Ma’aikatan Hukumar NIPOST Sun Ki Yarda Da Shugaban Da Tinubu Ya Nada

“Mahukuntan jami’ar na sun bayyana a fili cewa labarin karya ne kuma ba shi da tushe, don haka ya kamata jama’a su yi watsi da shi,” in ji Datti.

 

Advertisement

Ya kuma yi kira ga jama’a da su daina yada irin wannan jita-jita da bata da tushe bare makama.

A Wani labarin kuma Ma’aikatan Hukumar NIPOST Sun Ki Yarda Da Shugaban Da Tinubu Ya Nada

Advertisement

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

Advertisement

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending