News
Ma’aikatan Hukumar NIPOST Sun Ki Yarda Da Shugaban Da Tinubu Ya Nada
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ma’aikatan hukumar aikewa da sakonni ta Nijeriya NIPOST, sun rufe babban ofishin hukumar da ke Abuja, suna zanga-zangar nuna adawa da nadin Tola Odeyemi a matsayin babban jami’in gudanarwa a hukumar.
Cif Ajuri Ngelale, mai magana da yawun shugaban kasa, ya bayyana a makon da ya gabata cewa, shugaban kasa Bola Tinubu, ya yi wasu sauye-sauye a shugabancin hukumomin sadarwa da suka hada da NIPOST.
Majalisar Wakilan Kassr nan Zata Raba Sabbin Motoci Ga ‘Yan Majalisar
Sai dai jim kadan bayan da labarin nadin Odeyemi ya bulla, an samu rahotannin cewa an mayar da Adeyemi Adepoju, wanda aka kora daga mukamin babban jami’in gudanarwar humumar.
A cikin wani faifan bidiyo, an ga Adepoju yana jawabi ga wasu ma’aikata da suka yi ikirarin cewa Tinubu ya sake nada shi.
Sai dai a ranar Litinin ma’aikatan sun yi zanga-zangar sun kuma hana sabuwar shugabar hukumar ta NIPOST shiga ofishin hukumar, inda suka ce nadin nata ya saba wa muradinsu.
Ma’aikatan, wadanda suka ce sun fi son Adepoju, sun rera wakokin hadin kai da dauke da allunan nuna rashen amincewa da sabon nadin.
A wani labarin kuma Majalisar Wakilan Kassr nan Zata Raba Sabbin Motoci Ga ‘Yan Majalisar
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
