News
IBADAN: Hausawa Sun Yi Zanga-zanga Kan Danganta Su Da Satar Mutane
Wasu daga cikin al’ummar Hausawa mazauna Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, sun gudanar da zanga-zanga domin nuna rashin amincewarsu kan alaƙanta su da laifukan satar mutane da ke faruwa a jihar.
Masu zanga-zangar sun ce ba daidai ba ne a riƙa danganta dukkanin Hausawa da aikata laifuka saboda laifin wasu tsiraru.
Wannan zanga-zanga na zuwa ne makonni kaɗan bayan sace ɗalibai da malamai 46 a wani hari da aka kai makarantu uku a Ƙaramar Hukumar Oriire a jihar.
Al’ummar Hausawan sun buƙaci jama’a da hukumomi su guji yi musu kallon masu laifi saboda asalinsu ko ƙabilarsu, tare da jaddada cewa mafi yawan Hausawa mazauna jihar mutane ne masu zaman lafiya da bin doka.
Advertisements
