News
IBADAN: Hausawa Sun Yi Zanga-zanga Kan Danganta Su Da Satar Mutane
Wasu daga cikin al’ummar Hausawa mazauna Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, sun gudanar da zanga-zanga domin nuna rashin amincewarsu kan alaƙanta su da laifukan satar mutane da ke faruwa a jihar.
Masu zanga-zangar sun ce ba daidai ba ne a riƙa danganta dukkanin Hausawa da aikata laifuka saboda laifin wasu tsiraru.
Wannan zanga-zanga na zuwa ne makonni kaɗan bayan sace ɗalibai da malamai 46 a wani hari da aka kai makarantu uku a Ƙaramar Hukumar Oriire a jihar.
Al’ummar Hausawan sun buƙaci jama’a da hukumomi su guji yi musu kallon masu laifi saboda asalinsu ko ƙabilarsu, tare da jaddada cewa mafi yawan Hausawa mazauna jihar mutane ne masu zaman lafiya da bin doka.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News5 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
