News
Mata 7 Sun Rasa Ransu Yayin Da Wasu Suka Samu Raunuka A Lokacin Wata Zanga-zanga A Adamawa
Akalla mata bakwai suka rasa rayukansu, yayin da wasu goma sha ɗaya suka samu raunuka a lokacin wata zanga-zanga da aka gudanar a jiya a ƙaramar hukumar Lamurde ta jihar Adamawa, a shiyar Arewa maso gabashin Najeriya.
Rahotanni daga jaridar Daily Trust sun nuna cewa matan, wadanda ke riƙe da ganyayyaki, sun gudanar da zanga-zangar ne domin nuna rashin jin daɗinsu kan jinkirin isowar sojoji wajen kwantar da tarzomar da ta ɓarke tsakanin ƙabilar Bachama da Chobo a yankin.
Gwamnan Jihar Osun Adeleke Ya Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyyar Accord
A cewar wasu majiyoyi, yayin da ake ta tattaunawa tsakanin sojojin da matan masu zanga-zangar, jami’an sojin sun yi harbi cikin dandazon masu zanga-zangar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mata huɗu nan take, sannan wasu uku suka mutu a asibiti. Haka kuma wasu mutum goma sha ɗaya suka ji rauni.
Hakimin Gyawana na ƙaramar hukumar Lamurde, Agoso Bamaiyi, ya tabbatar da cewa waɗanda suka samu raunuka suna kwance a babban asibitin Numan, inda jami’an lafiya suka bayyana cewa wasu na cikin mawuyacin hali.
Bayan faruwar lamarin, Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, ya sanya dokar hana fita na sa’o’i 24 a yankin Lamurde, tare da umurnin gaggauta maido da zaman lafiya ta hanyar jami’an tsaro.
