Connect with us

News

Jihohi 7 Za Su Fuskanci Katsewar Wutar Lantarki Na Tsawon makonni A Arewacin Najeriya 

Published

on

Duk da rashin wuta, kamfanin lantarki na Kaduna ya buƙaci a biya kuɗin wuta

Masu amfani da wutar lantarki a jihohi bakwai — Filato, Gombe, Bauchi, Borno, Adamawa, Taraba da Yobe — za su fuskanci katsewar wuta na tsawon makonni sakamakon shirye-shiryen katse wuta a layin wutar lantarki na Jos–Gombe mai ƙarfin 330kV.

Hukumar dake Kula da Tsarin Wutar Lantarki ta Nijeriya ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, inda ta ce katsewar za ta gudana daga ranar 9 ga Afrilu zuwa 22 ga Mayu, 2026.

Advertisement

Amurka Ta Bai Wa Jami’anta Umarnin Barin Ofishin Jakadancinta Na Nijeriya

A cewar hukumar, katsewar wutar za a rika yinta ne duk mako daga ranar Alhamis zuwa Lahadi, daga ƙarfe 9:00 na safe zuwa 6:00 na yamma.

Advertisement

Ta bayyana cewa an shirya katse wutar ne domin samar da damar girka kayan sadarwa na ‘fibre optic’ na karkashin kasa a kan layin wutar, a wani bangare na kokarin inganta tsarin wutar lantarki ta kasa.

“Hukumar Kula da Tsarin Wutar Lantarki ta Nijeriya na sanar da masu amfani da wutar a jihohin da abin ya shafa cewa za a katse wuta a layin Jos–Gombe 330kV daga ranar 9 ga Afrilu zuwa 22 ga Mayu, 2026.

Advertisement

“Wannan katsewar ya zama dole domin samar da damar girka kayan fibre optic na Optical Ground Wire a kan layin,” in ji sanarwar.

 

Advertisement

 

LEADSHIP

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending