News
Yanzu-Yanzu: Sojoji Sun Tabbatar Da Cewa Su ne Suka Yi Luguden Bama bamai ga Mazauna Wani Kauye a Kaduna

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar sojin Najeriya ta ce ita ce ta kai harin bam da aka kai kan mutanen kauyen a yayin bikin Maulud da aka yi a Tudun Biriin da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.
Sai dai rundunar sojin ta ce harin da aka kai ta sama ba bisa ka’ida ba ne, inda ta ce jami’an na kai hare-haren ne kan ‘yan ta’adda.
Rundunar Sojin Saman Najeriya ta musanta harin bam a kauyen Kaduna
Kimanin mazauna garin 30 ne ake fargabar sun mutu a harin da aka kai ta sama a daren Lahadi.
kwamishinan Samuel Aruwan, mai kula da Ma’aikatar tsaron cikin gida da harkokin cikin gida ta jihar Kaduna, ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin , inda ta ce rundunar sojin kasar ta dauki alhakin wannan mummunan lamari kamar yanda Jaridar Daily Trust ta ruwaito
“Gwamnatin jihar Kaduna ta samu bayanai kan harin da aka kai daren Lahadi wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan kasar da dama tare da jikkata wasu.
A taron da mataimakiyar gwamnan jihar, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ta jagoranta, wanda ya samu halartar shugabannin hukumomin tsaro, na addini da na gargajiya, rundunar sojin Najeriya ta bayyana halin da ake ciki wanda ya kai ga harin da ba a so.
