News
Ganduje Ya Nesanta Kansa Da Rahoton Da Aka Danganta Masa Kan Kudaden Gwamnatin Kano
Advertisements

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa kuma shugaban hukumar gudanarwar FAAN, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya nesanta kansa da rahoton da ke cewa ya soki gwamnatin jihar Kano kan yadda take kashe kudaden jama’a.
Advertisements
Advertisements
A wata sanarwa da shugaban ma’aikatansa, Comrade Muhammad Garba ya sanya wa hannu, Ganduje ya bayyana rahoton a matsayin na kage kuma mara tushe, yana mai cewa bai taba yin irin wannan hira ba.
Advertisements
Za’a fuskanci Katsewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi A Ranar Lahadi
Advertisements
Advertisements
Ya bukaci jama’a da su yi watsi da rahoton, tare da bayyana cewa ana binciken wadanda suka kirkiri labarin domin daukar matakin doka a kansu.
Advertisements
