Sports
Dan Kwallo Ya Mutu Ana Tsaka Da Atisaye A Filin Wasa
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Rahotanni sun ce dan wasan yana atisaye da wasu ‘yan wasan kwallon kafa a ranar Asabar lokacin da lamarin ya faru.
Lokacin da abokan wasansa suka ga matashin mai shekaru 34 a duniya ya fadi, sai suka garzaya da shi asibitin jihar da ke Ijebu-Ode.
Sai dai duk da irin kokarin da kwararrun asibitin suka yi, an tabbatar da rasuwarsa a ranar da aka kai shi asibitin.
Kakakin ‘yansandan jihar, Omolola Odutola, a ranar Talata ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma bayyana cewa, dan uwan marigayin, Ganiyu Adebisi, ya karbi gawar matashin don birne ta.
“Dan uwansa ya zo ne ya kai rahoton faruwar lamarin a sashenmu na Igbeba. Iyayensa sun ce ba sa son wani bincike kuma suna son a birne marigayin kamar yadda Addinin Musulunci ya tanadar, ”in ji Odutola.
A wani labarin kuma Yanzu Haka Masu Zanga Zanga Sun Nufi Majalisar Wakilan Najeriya domin nuna bacin ransu kan harin da sojoji Sukayi
Shugaba Joe Biden na Amurka ya ce ƙoƙarin da Donald Trump ke yi na yunkurin komawa Fadar White House na daga cikin abin da ya karfafa sake tsayawarsa neman wa’adin mulki karo na biyu.
Da ya ke jawabi a gangamin tara kudin kamfe, Biden ya ce bai kamata su bar Donald Trump ya yi nasara ba.
Wanna ne karon farko da joe Biden ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takarar shugaban Ƙasa a karo na biyu.
Don haka kai tsaye kan burin tsohon shugaban, ya ce idan Trump ba zai sake tsayawa takarar ba shi ma baya tunanin zai tsaya.
An tambayi Biden ko zai ci gaba da tsayawa takarar idan Trump ya janye, sai shugaban Amurkar mai shekaru 81 ya ce ba zai tsaya takara ba.
