Connect with us

News

An Samu Rahoton Tashin Gobara A Jahar Kaduna Sau 33 Cikin Watan Nuwamba 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Hukumar kashe gobara ta jihar Kaduna ta ce ta samu barkewar gobara sau 33 da kuma mutuwar mutum daya a watan Nuwamba a fadin jihar.

Daraktan hukumar Mista Paul Aboi ne ya bayyana haka a wata hira da manema labarai a ranar Talata a Kaduna.

Advertisement

An Kama Ma’auratan Da Suka Sayi Jaririn Wata Daya A Kan 30,000

Aboi ya ce hukumar ta ceto mutane hudu yayin da wasu hudu suka samu raunuka sakamakon lamarin,wanda ya lakume dukiyoyin bayin Allah da dama.

 

Advertisement

Hukumar ta ceci kadarorin da suka kai kimanin Naira miliyan 963 daga konewa yayin da aka lalata dukiyar da ta kai Naira miliyan 406 a cikin lokacin da ake nazari, inji shi.

Daily Post ta ruwaito cewarsa, rashin kulawa da amfani da na’urorin lantarki ne ya haifar da barkewar cutar ya bukaci mazauna yankin da su dauki matakan kariya domin kaucewa afkuwar gobara.

Advertisement

Aboi ya bayyana cewa hukumar ta himmatu wajen rage barkewar gobara ta hanyar kaddamar da wani gagarumin shiri na duba rigakafin gobara tare da kaddamar da sabunta takardun shaidar kashe gobara a wuraren kasuwanci a jihar.

A wani labarin An Kama Ma’auratan Da Suka Sayi Jaririn Wata Daya A Kan 30,000

Advertisement

Yanzu dai Babu wani Abu da al’ummar jihar kano ke yawan tattaunawa akansa Kamar batun shari’ar zaben gwamnan jihar.

Wakilin jaridar Inda Ranka Yasir Sani Abdullahi ya gano yadda kusan da yawa daga cikin wuraren zaman alumma da kasuwanni harma da ofisoshin gwamnatin da masu zaman Kansu, Babu wani batu da yafi daukar hankali Kamar batun shari’ar

Advertisement

Magoya bayan dukkan babgarorin manyan jam’iyyun APC Dana NNPP na bugar kirgin samun nasara a kotun koli.

Jam’iyyar APC na da kwarin guiwar cewa Zata Kara samun nasara a kotun koli kasancewar kotun farko da ta biyu duka ta Bata nasara

Advertisement

Sai dai jam’iyyar NNPP Bayan korafe korafe da tayi akan hukunce hukunce na kotun baya, yanzu ta bayyana kwarin guiwar da take dashi na samun nasara a kotun koli.

Al’ummar jihar kano da dukkan bangarorin manyan jam’iyyun APC Da NNPP na dakon hukuncin na karshe na kotun koli wadda ake saran Zata yanke cikin karshen watan Nan, shi zai kawo karshen jayayya da kowane bangare keyi a jihar kano.

Advertisement

Masu iya magana na cewa Shari’a mace ce da ciki ba’asan wa Zata Haifa ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending