News
Ramadan: Ɗangote ya ƙudiri aniyar tallafa wa mabuƙata da kayan abinci
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Hamshaƙin mai arzikin nan Alhaji Aliko Ɗangote mai son tallafawa al’ummar ƙasar nan don sauƙaƙa musu daga halin matsin tattakin arzikin da ake ciki zai tallafawa mabuƙata da kayan abinci kyauta don yin azumin watan Ramadan cikin walwala.
Ɗiyarsa Hajiya Fatima Aliko Ɗangote ce ta bayyana hakan, yayin wani taron ganawa da ‘yan jaridu na Arewacin Nijeriya da ya gudana a birnin Kano.
TIRƘASHI: Wasu kaya sai Amale ! Idan Rana ta fito ai tafin hannu baya iya rufeta.
Hajiya Fatima ta ce mahaifinta ya jima yana gudanar da ayyuka domin kyautata rayuwar al’ummar Jihar Kano, shi ya sa a wannan lokaci ya ƙudiri aniyar tallafawa mabuƙata da kayan abinci sakamakon halin qunci da matsin rayuwar da ake ciki.
Ga waɗanda ke bibiyar ayyukan jinƙai na Gidauniyar Ɗangote suna sane da yadda ake gudanar da ayyukan inganta rayuwar jama’a a asibitoci baya ga bayar da abinci ga mabuƙata tsawon shekaru.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
