News
Yan Sanda Sun Kama Mutum 15 Da Ake Zargi Da Fasa Rumbun Ajiye Kayan Abinci
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar ‘yansanda a birnin tarayya Abuja, ta ce ta kama wasu mutane 15 da ake zargi da lalata wani rumbun ajiyar kaya na hukumar raya babban birnin tarayya Abuja.
Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sanda a birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ce ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar ranar Lahadi a Abuja.
Ramadan: Sarkin Kano Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Da Su Rage Farashin Kayan Abinci
Ta ce, wasu jami’an tsaro biyu da jami’an kula da rumbunan da ke aiki a wurin suna daga cikin wadanda ake zargin kan barna a rumbun ajiyar da ke unguwar Tasha a Abuja.
Adeh ta ce an kwato buhunan masara guda 26 da Babura biyar da kuma wasu kwanukan rufi na aluminium daga hannun wadanda ake zargin.
“Rundunar ‘yansanda a birnin tarayya Abuja ta samu rahoto game da harin da aka kai a unguwar Tasha da ke Abuja, a ranar 3 ga Maris.
“Harin ya haifar da barna tare da wawashe kayan ajiyar da ke wurin
Leadership ta ruwaito cewa sashen bunkasa noma da raya karkara na FCTA, ya tabbatar da sace kaya a ma’ajiyar a ranar Lahadi.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
