Connect with us

News

Gwamnan Jihar Borno BabaganaZulum Ya Bukaci Sojojin Nijeriya Da Su Kafa Sansani A Dajin Sambisa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum ya bukaci sojojin Nijeriya da su kafa sansanin soji a dajin Sambisa, domin dakile ayyukan ‘yan ta’adda yadda ya kamata.

Leadership ta ruwaito cewa ya bayyana hakan ne a wata ziyarar ban girma da mambobin kwamitin majalisar wakilai kan harkokin soji suka kai masa, ranar Laraba a Maiduguri.

 Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Naɗin Lawan Badamasi Matsayin Sabon Kwamishinan Zaɓe Na Jihar Kano

Gwamnan ya kuma bukaci sojojin da su kafa sansanin soji a gabar tafkin Chadi da kuma tsaunin Mandara wanda har yanzu ya ci gaba da zama mafakar ‘yan ta’adda.

Ya bukaci Majalisar Dokoki ta kasa da ta tabbatar da samar da isassun makamai don magance rashin tsaro.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending