News
Yadda Wutar lantarki ta hallaka wani barawon tiransifoma
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wani matashi da har yanzu ba a tantance ba ya gamu da ajalinsa a kusa da cibiyar shirya jarabawar shiga jami’a (JAMB) da ke Otukpo, hedikwatar karamar hukumar Otukpo ta jihar Benue.
Shi dai wanda ake zargin barawon ne ya gama lalata na’urar taransfoma da ke kan wani wuri kafin daga bisani wutar lantarki ta kama shi, inda kwatsam Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Jos (JEDC) ya dawo da wuta wadda tayi sanadiyar ajalinsa.
DAILY POST ta tattaro cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a.
Har ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, jami’an rarraba wutar lantarki na ci gaba da zakulo gawar wanda ake zargin.
Wata majiya ta ce, “Mun zo ne da safiyar yau, muka tarar da gawar an dakatar da ita daga sandar wutar lantarki a wani tiransfoma da kayan aiki a hannunsa.
