News
Karan farko jigo a jam, iyyar APC ya magantu Kan kuncin rayuwa da al, ummar Nigeria ke ciki
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na Arewa maso Yamma, Dakta Salihu Lukman, ya koka kan yadda Shugaba kasa Bola Tinubu ya jefa al’ummar ƙasar nan cikin wani yanayi na ƙunci sabida manufofinsa wanda hakan ke kara ta’azzara yanayin kuncin rayuwar ga ƴan Nijeriya.
Lukman a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi ya yi mamakin irin yadda Tinubu ya ke nuna halin rashin ko in kula wajen gyara matsalolin ƙasar nan.
Ya ce ko ta fuskar gyara kalubalen da ƴan Najeriya ke fuskanta, Gwamnati ta nuna rashin sanin makama wajen gudanar da Gwamnati.
Tsohon jigon na APC ya ce sama da shekara daya magana ɗaya Shugaba Tinubu yake yi, tare da rashin kyakkyawar manufa da tsari wajen ciyar da tattalin arzikin Najeriya gaba.
Lukman ya ce “A kowace rana rashin tabbas na Gwamnati na ƙara fitowa fili.
Wannan yanayin da ya jefa al’ummar kasar cikin wani yanayi na rashin tabbas wanda ya ƙara haddasa tabarbarewar tattalin arzikin ƴan Nijeriya, shin wane shiri ne Shugaba Tinubu ya yi na gyara matsalar
daga karshe dai ya dasa ayar tambaya akan salon milkin Bola tinubu na rashin kyawawan manufa a sha,anin mulkin sa
