Connect with us

News

Zargin Ta’addanci: ‘Zamu Tafi Yajin Aiki Idan ‘Yan Sanda Sun Tsare Ajaero’ – Kungiyar NLC

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Ƙungiyar kwadago ta kasa NLC,ta yi barazanar tsunduma yajin aiki a faɗin ƙasar nan idan har rundunar ƴan sandan Nijeriya ta tsare shugabanta na kasa, Joe Ajaero.

Advertisement

Ƙungiyar tayi barazanar shiga yajin aikin ne a yau Talata a shelkwatar ta bayan taron gaggawa da kwamitin ƙoli na kungiyar na kasa ya gudanar don tattauna gayyatar da ‘yan sanda suka yiwa shugaban NLC kan zargin daukar nauyin ta’adannci.

Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Jihar Kano Za Ta Gudanar Da Bincike Kan Zargin Badakalar Wasu Kudade

Ƙungiyar ta ce Ajaero zai amsa gayyatar ‘yan sandan sai dai mai bai wa kungiyar shawara a fannin shari’a zai nemi karin lokaci kafin shugaban na NLC ya bayyana gaban rundunar yan sandan.

Advertisement

Comrade Ado Kabiru Sani, mataimakin shugaban NLC na kasa ya bukaci ma’aikata da su zauna da shirin ko ta kwana idan ‘yan sanda suka tsare Ajaero.

 

Advertisement

Channels

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending