News
Zargin Ta’addanci: ‘Zamu Tafi Yajin Aiki Idan ‘Yan Sanda Sun Tsare Ajaero’ – Kungiyar NLC
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Ƙungiyar kwadago ta kasa NLC,ta yi barazanar tsunduma yajin aiki a faɗin ƙasar nan idan har rundunar ƴan sandan Nijeriya ta tsare shugabanta na kasa, Joe Ajaero.
Ƙungiyar tayi barazanar shiga yajin aikin ne a yau Talata a shelkwatar ta bayan taron gaggawa da kwamitin ƙoli na kungiyar na kasa ya gudanar don tattauna gayyatar da ‘yan sanda suka yiwa shugaban NLC kan zargin daukar nauyin ta’adannci.
Ƙungiyar ta ce Ajaero zai amsa gayyatar ‘yan sandan sai dai mai bai wa kungiyar shawara a fannin shari’a zai nemi karin lokaci kafin shugaban na NLC ya bayyana gaban rundunar yan sandan.
Comrade Ado Kabiru Sani, mataimakin shugaban NLC na kasa ya bukaci ma’aikata da su zauna da shirin ko ta kwana idan ‘yan sanda suka tsare Ajaero.
-
News6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News2 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
