Connect with us

News

Seaman Abbas Haruna: Hedikwatar Tsaron Najeriya Ta Fara Bincike Kan Tsare Shi Na Tsawon Shekaru Shida

Published

on

9b8dd982 67f0 4fa8 bd5d 76b826e2aa41 cx0 cy1 cw0 w408 r1 s

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta bayar da umarni kan a ƙaddamar da bincike dangane da tsare sojan ruwan nan na Najeriya Seaman Abbas Haruna, kamar yadda sanarwar da ta fitar ta bayyana.

Advertisement

A ƙarshen makon da ya gabata ne aka ga wani bidiyo na yawo a kafofin sada zumunta inda aka ga matar Seaman Abbas tana zargin wani babban soja da tsare mijinta tsawon shekaru shida.

Kamfanin NNPCL zai sayar da fetur ɗin Dangote kan N1,019 a Borno, N999 a Sokoto, Kano da Kaduna

“Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kula da wani bidiyo wanda ke yawo kan tsare wani sojan ruwa Seaman Abbas Haruna tsawon shekara shida.

Advertisement

“Hedikwatar Tsaron Najeriya na son bayar da tabbaci ga jama’a kan cewa sojojin Najeriya za su ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci, gaskiya, da bin doka da oda. Tsarin kotun soja duk da cewa ana takatsantsan, ana tabbatar da adalci da ba kowa dama bisa ka’idojin aikin soja da doka,” in ji sanarwar.

Haka kuma sanarwar ta ƙara da cewa tuni babban hafsan tsaron ƙasar Janar Christopher Musa ya bayar da umarni kan gudanar da bincike kan lamarin, da kuma bayyana sakamakon binciken ga jama’a.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending