News
Innalillahi Wainnailaihi Rojiun : Allah Ya Yi Wa Mawakin Hausa El-mu’az Rasuwa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Allah ya yi wa fitaccen mawaƙin Hausa a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, El-mu’az Muhammad Birniwa, rasuwa kamar yanda Jaridar LEADSHIP HAUSA ta ruwaito a shafin ta sada zumunta na Facebook
Kafin rasuwar haziƙin mawakin ya yi waƙoƙi da dama, kuma ɗan asalin ƙaramar hukumar Birniwa ne ta jihar Jigawa, an haife shi a jihar Kaduna inda anan ya taso, ya gudanar da rayuwarsa. Muna addu’ar Allah ya gafarta masa.
Advertisements
