News
Gwamna Kano Ya Umurci Kwamishinoni da Aka Canza Su Miƙa Dukkanin Takardun Da Suka Kamata Kafin Talata
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya umurci dukkan kwamishinoni da aka sake musu wuraren aiki su tabbatar da gudanar da cikakken bayanai kafin ƙarshen ranar Talata, 17 ga Disamba, 2024.
Da yake magana ta bakin mai magana da yawunsa, Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa, Gwamnan ya bayyana cewa sauye-sauyen cikin majalisar zasu fara aiki ne gaba ɗaya a taron majalisa na gaba da za a yi ranar Laraba, 18 ga Disamba, 2024.
Ya jaddada muhimmancin kammala dukkan tsare-tsaren miƙa aiki kafin wannan lokaci.
“Dukkan kwamishinonin da sauyin ya shafa su miƙa wuya da sauya aiki tsakanin ranar Litinin, 16 da Talata, 17 ga Disamba, 2024,” in ji sanarwar.
Gwamnan ya ƙara jawo hankalin mambobin majalisar zartarwa ta jihar da su ƙara himma tare da rungumar ƙwazo, da jajircewa don ci gaba da tallafa wa gwamnatinsa wajen yi wa al’ummar Jihar Kano hidima.
