News
Watsi Da Irin Su El Rufai, Ba Alheri Ba Ne – Igbokwe
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Wani tsohon na hannun daman shugaban Najeria Bola Ahmed Tinubu Joe Igbokwe ya bayyana damuwa a kan yadda jam’iyyar APC ta yi watsi da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El Rufai.
Igbokwe wanda ke cikin tawagar yakin neman zaben Tinubu lokacin da suka yi ta fadi tashi da El Rufai wajen ganin jam’iyyar APC ta samu nasara yace duk cikin ministocin gwamnatin Tinubu babu kwarare, mai ilimi da wayo da kokari da kuma kwarewa kamar El Rufai, saboda haka babu dalilin watsi da shi.
DA DUMI DUMI: Kungiyar Kwadago Ta Sanar Da Ranar Fara Yajin Aiki A Fadin Najeriya
‘Dan siyasar ya ce kuskure babba watsi da irin su El Rufai yayin da ya zargi wasu mutane da hana tantance shi a matsayin minista, tare da karawa da cewar barin sa ya fada cikin ‘yan adawa ba zai yiwa jam’iyyar su alheri ba.
Daily Trust
