Connect with us

News

Yadda Kotu Ta Tuɓe Wa Sarkin Ebira Sarauta A Kogi

Published

on

An kama lauyan bogi ana tsaka da shari'a a kotu

DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO 

Wata babbar kotu a jihar Kogi da ke zaune a Lokoja ta sauke Alhaji Ahmed Muhammed Tijani Anaje daga muƙamin Ohinoyin Ebira.

Advertisement

Anaje ya samu naɗin sarautar ne a watan Janairu na 2024 daga tsohon gwamnan jihar, Alhaji Yahaya Bello, kafin ƙarshen wa’adin mulkinsa.

Kotu Ta Yanke Wa Wasu Mutum Biyar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kano

Sai dai a zaman kotu da aka yi a yau Litinin, mai shari’a Salisu Umar ya bayar da umarnin dakatar da Anaje daga ci gaba da bayyana kansa a matsayin sarkin Ebira.

Advertisement

Duk da cewa cikakken bayani kan hukuncin bai fito ba tukuna, an ruwaito cewa ƙarar da ke ɗauke da lamba HCO/05C/2024, Dr. Barnabas Adeku Ojiah da wasu mutane biyu suka shigar da ita kan gwamnan jihar Kogi na da nasaba da hukuncin.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

WIKKI TIMES 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending