News
Yadda Kotu Ta Tuɓe Wa Sarkin Ebira Sarauta A Kogi
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Wata babbar kotu a jihar Kogi da ke zaune a Lokoja ta sauke Alhaji Ahmed Muhammed Tijani Anaje daga muƙamin Ohinoyin Ebira.
Anaje ya samu naɗin sarautar ne a watan Janairu na 2024 daga tsohon gwamnan jihar, Alhaji Yahaya Bello, kafin ƙarshen wa’adin mulkinsa.
Kotu Ta Yanke Wa Wasu Mutum Biyar Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Kano
Sai dai a zaman kotu da aka yi a yau Litinin, mai shari’a Salisu Umar ya bayar da umarnin dakatar da Anaje daga ci gaba da bayyana kansa a matsayin sarkin Ebira.
Duk da cewa cikakken bayani kan hukuncin bai fito ba tukuna, an ruwaito cewa ƙarar da ke ɗauke da lamba HCO/05C/2024, Dr. Barnabas Adeku Ojiah da wasu mutane biyu suka shigar da ita kan gwamnan jihar Kogi na da nasaba da hukuncin.
-
News5 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
