Connect with us

News

Dakarun Soji Sun Kashe Wasu Fitattun Shugabannin ‘Yan Bindiga Guda Uku A Zamfara

Published

on

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 101 Sun Kama Wasu 182 A Cikin Mako Daya

Dakarun sojin Najeriya sun kashe wasu fitattun shugabannin ‘yan bindiga guda uku — Auta Jijji, Dankali da Sagidi — a wani samame da suka kai a kauyen Mai Kwanugga da ke Karamar Hukumar Talata Mafara a Jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru da misalin karfe 1:30 na dare ranar Laraba, 1 ga watan Mayu, lokacin da dakarun da ke sintiri suka gamu da daruruwan ‘yan bindiga dauke da makamai suna kai hari kan kauyen.

An ce ‘yan bindigar sun shiga kauyen ne a kan babura suna harbi da kona gidaje. Sai dai sojojin sun fatattake su tare da kashe da dama daga cikinsu, ciki har da shugabanninsu guda uku da hukumomi suka dade suna nema ruwa a jallo.

Sojoji sun ce sun kwato bindigogi da dama da kuma harsasai daga wajen ‘yan ta’addan.

Bayanai sun ce mutum biyu daga cikin mazauna kauyen sun jikkata sakamakon harbin bazata.

A wani bangare, dakarun soji sun tarwatsa wata zanga-zanga a Kaura Namoda da wasu matasa suka yi sakamakon yawaitar hare-haren ‘yan fashi da garkuwa da mutane a yankin.

Advertisement

Matasa sun toshe hanya da tayoyi suna neman gwamnati ta dauki mataki. Sai dai jami’an tsaro sun shawo kan lamarin ba tare da amfani da karfi ba.

Rundunar soji ta ce yanzu an samu kwanciyar hankali a yankunan da lamarin ya faru, kuma suna ci gaba da sintiri domin hana faruwar wani abu makamancin haka.

Kisan Auta Jijji, Dankali da Sagidi na daga cikin manyan nasarori da dakarun Najeriya suka samu a yaki da ‘yan ta’adda a Arewa maso Yamma.

 

ZAGAZOLA MAKAMA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending